{"id":3975,"date":"2025-09-21T12:13:16","date_gmt":"2025-09-21T12:13:16","guid":{"rendered":"https:\/\/taskarnasaba.com.ng\/?p=3975"},"modified":"2025-09-21T12:15:20","modified_gmt":"2025-09-21T12:15:20","slug":"asali-da-tarihin-jukunawa-masarautar-wukari-a-idon-duniya","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975","title":{"rendered":"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya"},"content":{"rendered":"\n<p><em><strong>Wukari<\/strong><\/em><em>, kamar yadda aka fi kiranta, ita ce Hedikwatar Masarautar<\/em><em><strong> Wukari<\/strong><\/em><em>. Asalin sunanta shi ne &#8216;<\/em><em><strong>Ukari<\/strong><\/em><em>,&#8217; wacce kuma kalma ce ta <\/em><em><strong>Jukunanci<\/strong><\/em><em>, wacce ke da ma\u2019anar; &#8216;Ka fifita&#8217; (you have surpassed).<\/em><\/p>\n\n\n\n<p><em>Masarauta ce da aka kafa ta a shekarar 1596 bayan rushewar Daular<\/em><em><strong> Kwararrafa<\/strong><\/em><em>.<\/em><\/p>\n\n\n\n<p>&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp; <strong>TUSHE<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Bayan rushewar Daular <strong>Kwararrafa<\/strong> wacce ke da Hedikwata a <strong>Api<\/strong>, sai <strong>Jukunawa<\/strong> wa\u0257anda suke tun asali su ne ke shugabanta waccar Daula ta <strong>Kwararrafa<\/strong> suka matsa gaba zuwa wannan bigire, suka kafa garin da a yanzu ake kira <strong>Wukari<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>Ita kuwa wannan kalma ta <strong>Wukari<\/strong>, asalinta shi ne <strong>Ukari<\/strong>, wacce kuma kalma ce ta <strong>Jukunanci<\/strong> mai ma\u2019ana ta, &#8216;ka fifita&#8217; (you have surpassed).<\/p>\n\n\n\n<p>Sarkin <strong>Jukunawa<\/strong> na 40, <strong>Aku Uka Katakpa<\/strong>, shi ne ya jagoranci wannan \u0199aura a cikin shekarar 1596 (Adamu, 2016; Oleyede, 1996). Dukkan wanda ke shugabantar wannan Masarauta, shi ake kira &#8216;<strong>Aku Uka<\/strong>,&#8217; kalmomin da ke da ma\u2019ana ta &#8216;Sarkin da ya fifici kowane Sarki a Duniya&#8217;; wato sarkin da ya fi kowane Sarki a Duniya (Adamu, 2016).<\/p>\n\n\n\n<p>Wannan gari shi ne ya zamo tubulin canjin tarihin <strong>Jukunawa<\/strong>, ya kuma zama sabuwar Hedikwatar <strong>Daular Jukunawa<\/strong> zalla, a maimakon Daular ha\u0257aka ta <strong>Kwararrafa<\/strong> da <strong>Jukunawa<\/strong> suka shugabanta wacce ke \u0199unshe da mabambantan yaruka.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>KWARARRAFA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p><strong>Kwararrafa<\/strong>, wata tsohuwar Daula ce da rukunin \u0199abilun da ake kira \u0198awancen-Kwa (Kwa-Group) suka kafa ta a yankin Arewacin <strong>Kogin Binuwai<\/strong>. Daula ce da wasu masana tarihi suke ganin an kafa ta a cikin \u0199arni na 14. Ta kuma yi sharafinta daga wannan \u0199arni har zuwa cikin \u0199arni na 17 (Dinslage da Leger, 1996). Haka nan, Okpeh da Ochefu (babu lokacin bugu) sun ambata cewa, tarihi ya tabbatar da samuwar wata Daula mai suna &#8216;<strong>Kwararrafa<\/strong>&#8216; a Arewa da <strong>Kogin<\/strong> <strong>Binuwai<\/strong>. Wannan Daula ta ha\u0257aka tsakanin wa\u0257annan \u0199abilu masu asali guda,\u00a0<strong>Jukunawa<\/strong>\u00a0ne suka shugabance ta.<\/p>\n\n\n\n<div class=\"wp-block-media-text is-stacked-on-mobile\"><figure class=\"wp-block-media-text__media\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" width=\"1025\" height=\"769\" src=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129-1025x769.jpeg\" class=\"wp-image-3979 size-full\" srcset=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129-1025x769.jpeg 1025w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129-300x225.jpeg 300w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129-768x576.jpeg 768w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129-1536x1152.jpeg 1536w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129-600x450.jpeg 600w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129.jpeg 2000w\" sizes=\"(max-width: 1025px) 100vw, 1025px\" \/><\/figure><div class=\"wp-block-media-text__content\">\n<p><em>Jukunawa su na gaisar da sarkinsu cikin girmamawa.<\/em><\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>ASALI<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Rubuce-rubuce masu tarin yawa, kamar irin su Dr. Dawuda (2011), Mac-Leva (2009), Okunna, Emman, Gausa, da Solomon, (2014), Ujorha (2012), Dinslage da Leger (1996), sun ruwaito cewa, yarurrukan da suka kafa wannan daular \u0199awance ta <strong>Kwararrafa<\/strong> daga Gabas suka fito tare da ayyana <strong>Yamen<\/strong> a matsayin tushen su.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>YARURRUKA<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Yarurrukan da suka ha\u0257u suka kafa wannan Daula ta ha\u0257aka su na da tarin yawa, amma ka\u0257an daga cikin su sun ha\u0257a<strong> da: Jukun, Igala,\u00a0Ibira, Idoma, Alago<\/strong> (Boumo, 2011; Onawo, 2016), Boumo (2011) ya \u0199ara da <strong>Nupe, Mada, Kantana, Rindre, Eggon, Bassa Nge da Bassa Komo. Onawo<\/strong> (2016), ya \u0199ara da <strong>Goemi, Migili, Etulu, Iyala da Aros. Dinslage da Leger<\/strong> (1996), kuma suka zayyano <strong>Kwami, Kupto, Kushi, Piya, Bole, Bantu, Bole, Ngamo, Karekare, Kirfi<\/strong>, da <strong>Galembi<\/strong>. <strong>Andoma<\/strong> na <strong>Doma<\/strong>; wato <strong>Onawo<\/strong> (2016), ya ce, <strong>Jukunawa<\/strong> su ne shugabanni tare da\u00a0<strong>Aku<\/strong>\u00a0a matsayin jagoran addini.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>YA\u0198U\u0198UWA<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Mutanen Daular <strong>Kwararafa<\/strong>, mutane ne masu matu\u0199ar jarumtaka wajen ya\u0199i, an ruwaito cewa, sun yi galaba a ya\u0199in da suka gwabza da manyan Masarautun <strong>\u0198asar Hausa<\/strong> wa\u0257anda suka ha\u0257a da\u00a0<strong>Kano<\/strong>,\u00a0<strong>Katsina<\/strong>,\u00a0<strong>Dutse<\/strong>, <strong>Ningi<\/strong>, da kuma\u00a0<strong>Zazzau<\/strong>\u00a0(Wikipedia, 2016; Northern Nigerian Publishing Company, 1970; Sanusi, 2009).<\/p>\n\n\n\n<p>Wannan magana, ana iya \u0199arfafarta da sunayen wasu unguwanni guda biyu da ke cikin garuruwan <strong>Kano<\/strong> da <strong>Zariya<\/strong>. A garin <strong>Kano<\/strong> akwai wata unguwa mai suna \u201c<strong>Yakasai<\/strong>,\u201d wacce ruwayar kunne-ya-girmi-kaka ta shaida mana cewa, kalma ce da ke nufin \u201cZa mu dawo ko muna dawowa\u201d wacce ta fito daga bakin su <strong>Jukunawa<\/strong> a lokacin da suka ci <strong>Kano<\/strong> da ya\u0199i. Haka nan kuma akwai unguwa mai suna \u2018<strong>Tudun Jukun<\/strong>\u201d a cikin garin <strong>Zariya<\/strong>. <\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>DUR\u0198USHEWA<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Rikicin shugabanci (tattaunawa da sarkin Pindiga), gujewa hare-hare daga daular <strong>Barno<\/strong> ta wani gefen, da kuma maya\u0199an <strong>Musulunci<\/strong> na\u00a0<strong>Daular Shehu Usmanu<\/strong> <strong>\u018aanfodiyo<\/strong>\u00a0daga wani gefen (David, 2013; Boumo, 2011), na daga cikin manyan dalilan da ya kawo \u0199auracewar wasu yarurrukan daga wannan yankin suka \u0199etara zuwa Kudu da Kogin na <strong>Binuwai<\/strong>.<\/p>\n<\/div><\/div>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>TARIHI<\/strong>N<strong> JUKUNAW<\/strong>A <\/p>\n\n\n\n<p><strong>Jukun<\/strong>, kalma ce da ke nufin \u2018Mutum\u2019 a yaren Jukunanci (Okunna da Gausa, 2014), kuma, yare ne da wasu jama\u2019a ke magana da shi.<\/p>\n\n\n\n<p>Haka nan, dukkan wanda ya gaji wannan yare ya zama <strong>Bajukune<\/strong>, jama\u2019unsu kuma, <strong>Jukunawa<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>Sun kasance Mutane masu kar\u0253ar ba\u0199i, son zaman lafiya, son jama\u2019a, biyayya, fafutikar \u0199watar \u01b4anci, sannan kuma a lokaci guda jarumai a fagen ya\u0199i (Taraba Online, 2014). Su na ya\u0199i da duk nau\u2019o\u2019in danniya da zalunci.<\/p>\n\n\n\n<p>Sun kafa Daular <strong>Kwararrafa<\/strong> tare da ha\u0257in guiwar wasu \u0199abilu da suka ha\u0257a da; <strong>Igala<\/strong>, <strong>Ibira<\/strong>, <strong>Nupe<\/strong> da sauransu.<\/p>\n\n\n\n<p><strong>Kwararrafa<\/strong>, Daula ce da ta yi ya\u0199i da wasu daga cikin manyan Daulolin <strong>\u0198asar Hausa<\/strong> kamar irin su <strong>Kano<\/strong>, <strong>Katsina<\/strong>, <strong>Zazzau<\/strong>, da sauransu.<\/p>\n\n\n\n<p>Daular da ta ruguje daga baya ta samar da sabuwar <strong>Daular Jukun<\/strong> Zalla da ke da Hedikwata a garin Wukarin Jihar <strong>Taraba<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>ASALI<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p><strong>Jukunawa<\/strong>, sun shigo garuruwan ba\u0199a\u0199e (Bilad Sudan) daga Gabas. A tattaunawar da muka yi da Mai Martaba Sarkin Pindiga, <strong>Alhaji Muhammad Seyoji Ahmad<\/strong>, a ranar 13\/02\/2017, ya shaida mana cewa, <strong>Jukunawa<\/strong> sun fito ne daga <strong>Yamen<\/strong>, suka shigo ta \u0198asar <strong>Sudan<\/strong> ta yau, in da suka yada zango a garin <strong>Kartum<\/strong> (Khartoum ta Sudan). Daga nan suka rankayo ta gefen <strong>Kogin Cadi<\/strong>, kama-kama har suka zo <strong>Dutsen<\/strong> <strong>Bima<\/strong>. Daga wannan Dutse na Bima ne suka rabu gida biyu; kashi \u0257aya daga ciki suka kama hanyarsu tiryan-tiryan har zuwa <strong>Dutsen Binga<\/strong>, in da suka kafa wani Gari wanda a yau ake kiransa da sunan <strong>Yalwa<\/strong>. Nan suka zauna a kan wannan Dutse har zuwa lokacin da Sarkin Gombe <strong>Umaru<\/strong> <strong>\u0198wairanga<\/strong> ya ci su da ya\u0199i, abin da ya haifar da tarwatsewar su zuwa wasu sassa na wannan yanki har zuwa kusa da <strong>Kogin<\/strong> <strong>Biniwai<\/strong> a wani yanki da ake kira <strong>Pi<\/strong>, wanda daga baya ya zama Hedikwatar Daular <strong>Kwararrafa<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>Dr. Dawuda (2011), da Mac-Leva (2009), sun ruwaito cewa, <strong>Jukunawa<\/strong> daga <strong>Yemen<\/strong> suka zo. Dr. Dawuda (2011) ya \u0199ara da cewa <strong>Jukanawa<\/strong> asalinsu <strong>Yahudawa<\/strong> ne saboda zuwan Yahudawa <strong>Najeriya<\/strong> har Garin <strong>Wukari<\/strong>, don gudanar da bincike kan \u0253araguzan kayan ya\u0199i da suke da ala\u0199a da su. Sannan kuma ya jaddada cewar, su <strong>Jukunawa<\/strong> su na da wani salon rubutun da yake kama da <strong>Hibiranci<\/strong> (Yaren Yahudu).<\/p>\n\n\n\n<p>Amma (Okunna, Emman, Gausa, da Solomon, 2014; Ujorha, 2012), sun ha\u0257u a kan cewa, asalin <strong>Jukunawa<\/strong> daga \u0198asar <strong>Misira<\/strong> (Egypt) suke. In da a Ujorha (2012), aka nuna cewa, akwai kamanceceniyar Al\u2019adu da Addini da Jukanawan <strong>Kona<\/strong> da mutanen tsohuwar <strong>Masar<\/strong>, duk da cewa takardar ta ruwaito Tsangayar Tarihi ta Kwalejin Gwamnatin Tarayya (Federal College of Education) da ke Jalingo ta danganta asalin nasu da <strong>Yamen<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>Sai kuma ra\u2019ayin Britannica (2010), da suka ambata cewa, <strong>Kwararrafa<\/strong> wata Daula ce mai \u0199arfi daga <strong>Sudan<\/strong>. Wannan ra\u2019ayi na Britannica (2010), ya samu \u0199arin haske daga (Okunna, Emman, Gausa, da Solomon, 2014) cewa, sun taso ne daga <strong>Gabas ta Tsakiya<\/strong> (Middle East) zuwa <strong>Sudan<\/strong> \u0257in.<\/p>\n\n\n\n<div class=\"wp-block-media-text is-stacked-on-mobile\"><figure class=\"wp-block-media-text__media\"><img decoding=\"async\" width=\"1025\" height=\"769\" src=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun18968388432744885221-1025x769.jpeg\" class=\"wp-image-3976 size-full\" srcset=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun18968388432744885221-1025x769.jpeg 1025w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun18968388432744885221-300x225.jpeg 300w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun18968388432744885221-768x576.jpeg 768w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun18968388432744885221-1536x1152.jpeg 1536w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun18968388432744885221-600x450.jpeg 600w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun18968388432744885221.jpeg 2000w\" sizes=\"(max-width: 1025px) 100vw, 1025px\" \/><\/figure><div class=\"wp-block-media-text__content\">\n<p><em>Jukunawa a cikin shigar al&#8217;ada. <\/em><\/p>\n<\/div><\/div>\n\n\n\n<p>Saboda haka dai idan muka tattara wa\u0257annan bayanai sai muga cewa, asalin <strong>Jukunawa<\/strong> daga <strong>Gabas ta Tsakiya<\/strong> ne, suka zo suka zauna a <strong>Sudan<\/strong> tun cikin \u0199arni na hu\u0257u, sannan suka shigo \u0198asar Ba\u0199a\u0199e, in da suka fara yada zango a <strong>Kukawa<\/strong>, sannan suka koma <strong>Ngazargamu<\/strong>, sai kuma <strong>Dutsen<\/strong> <strong>Mandara<\/strong>, daga nan sai <strong>Mubi<\/strong> ta tsohuwar Jihar <strong>Gwangola<\/strong> wacce yanzu ta ke cikin Jihar Adamawan Najeriya, sai kuma garin <strong>Kilba<\/strong>, sai <strong>Kogin Hawal<\/strong> duk a Jihar <strong>Adamawa<\/strong> ta yau. Sai kuma suka zarce zuwa <strong>Shane<\/strong>, daga nan sai <strong>Pindiga<\/strong>, wa\u0257anda su kuma a yau suke cikin Jihar <strong>Gombe<\/strong>. Daga nan sai <strong>Gwana<\/strong> ita kuma a Jihar <strong>Bauchi<\/strong>, in da daga \u0199arshe suka yada zangonsu na \u0199arshe a Garin <strong>Wukari<\/strong> wacce ta zama babban garinsu har zuwa yau \u0257in nan (2025). Shi Garin <strong>Wukari<\/strong> yanzu ya na cikin Jihar <strong>Taraba<\/strong>, da ke Arewa maso Gabashin <strong>Najeriya<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp; <strong>RABE-RABEN JUKUNAWA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Gamgum (2015), ya kawo cewa, daga \u0199arni na ashirin zuwa yau, Jukunawa sun rarrabu zuwa kashe-kashe kamar haka:<\/p>\n\n\n\n<ul class=\"wp-block-list\">\n<li><strong>Jukunawan Asali<\/strong><\/li>\n<\/ul>\n\n\n\n<p>Wa\u0257annan su ne wa\u0257anda ba su da wani yare in ban da Jukunanci; su ne dukkanin wani mutum wanda iyayensa da kakaninsa Jukunawa ne sannan kuma ba shi da wani yare sai Jukunanci.<\/p>\n\n\n\n<ul class=\"wp-block-list\">\n<li><strong>Jaukunawan Dole<\/strong><\/li>\n<\/ul>\n\n\n\n<p>Wa\u0257annan su ne Jukunawan da su na da yarensu na asali wanda ba Jukunanci ba, amma saboda wasu dalilai suka saka su zama Jukunawa. Dolen da ake nufi a nan ta na iya zama; ta fuskacin ya\u0199i kamar Bayi da ake kamawa lokacin ya\u0199i ko kuma \u01b4an-ci-rani da ke zuwa cikin Jukunawa su zauna har wani lokaci mai tsawo da ka iya sakawa asalin nasu ya \u0253ace, saboda haka sai su zamo ba su da wani harshen-uwa sai Jukunanci.<\/p>\n\n\n\n<ul class=\"wp-block-list\">\n<li><strong>\u0198awayen Jukunawa<\/strong><\/li>\n<\/ul>\n\n\n\n<p>Wa\u0257annan su ne mutanen da suke da wani gado ta fuskacin yare da al\u2019adu da asali da Daula, kuma suka ci gaba da ri\u0199e wan\u0257annan al\u2019adu nasu, amma kuma akwai dangantaka ta \u0199ut-da-\u0199ut wacce ka iya zama ta zamantakewa, tattalin arzi\u0199i, siyasa, addini, ko wani abu daban, wacce suka \u0199ulla don cimma wannan manufar tare. Iri wa\u0257annan Jukunawa sun ha\u0257a har da wa\u0257anda suka yarda su bada Jiziya don ku\u0253uta daga hare-haren ya\u0199in abokan gaba na cikin \u0199arni na goma sha hu\u0257u. Misali, akwai wa\u0257anda suka nemi tallafin <strong>Jukunawa<\/strong> don samun kariya daga hare-haren ya\u0199u\u0199uwan <strong>Kano<\/strong>, <strong>Katsina<\/strong> da <strong>Zazzau<\/strong> a cikin shekarun \u0199arni na 14.<\/p>\n\n\n\n<p>A tattaunawarmu da Alhaji Gambo Garba, Galadiman Pindiga a ranar 13\/02\/2017, ya shaida cewa, Jukunawan Asali sun karkasu zuwa:<\/p>\n\n\n\n<ul class=\"wp-block-list\">\n<li>1. <strong>Jukun Wukari<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li>2. <strong>Jukun Pindiga<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li>3. <strong>Jukun Kona<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li>4. <strong>Jukun Kuteb<\/strong><\/li>\n<\/ul>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>YA\u0198U\u0198UWA<\/strong><\/p>\n\n\n\n<figure class=\"wp-block-image size-large\"><img decoding=\"async\" width=\"943\" height=\"454\" src=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/perennial-tiv-jukun-clashes-unsettle-taraba166542850096782615.jpg\" alt=\"\" class=\"wp-image-3980\" srcset=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/perennial-tiv-jukun-clashes-unsettle-taraba166542850096782615.jpg 943w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/perennial-tiv-jukun-clashes-unsettle-taraba166542850096782615-300x144.jpg 300w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/perennial-tiv-jukun-clashes-unsettle-taraba166542850096782615-768x370.jpg 768w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/perennial-tiv-jukun-clashes-unsettle-taraba166542850096782615-600x289.jpg 600w\" sizes=\"(max-width: 943px) 100vw, 943px\" \/><\/figure>\n\n\n\n<p><strong>Jukunawa<\/strong> wanda suka samo asali daga <strong>Kwararrafa<\/strong>, Mutane ne masu matu\u0199ar jarumtaka wajen ya\u0199i, a binciken da muka gudanar, mun ci karo da cewa, <strong>Jukunawa<\/strong> sun yi galaba a ya\u0199in da suka gwabza da manyan Daulolin <strong>\u0198asar Hausa<\/strong> wa\u0257anda suka ha\u0257a da <strong>Kano<\/strong>, <strong>Katsina<\/strong>, da kuma <strong>Zazzau<\/strong> (Northern Nigerian Publishing Company, 1970; Wikipedia, 2016).<\/p>\n\n\n\n<p>Wannan magana muna iya \u0199arfafar ta daga sunayen wasu unguwanni guda biyu da ke cikin garuruwan <strong>Kano<\/strong> da <strong>Zariya<\/strong>. A garin <strong>Kano<\/strong> akwai wata Unguwa mai suna \u201c<strong>Yakasai<\/strong>,\u201d wacce ruwayar kunne-ya-girmi-kaka ta shaida mana cewar, kalma ce da ke nufin \u201cZa mu dawo, ko muna dawowa,\u201d wacce ta fito daga bakin su <strong>Jukunawa<\/strong> a lokacin da suka ci <strong>Kano<\/strong> da ya\u0199i. Haka nan kuma akwai Unguwa mai suna <strong>Tudun Jukun<\/strong> a cikin Garin <strong>Zariya<\/strong>, wacce ita ma <strong>Jukunawa<\/strong> suka kafa ta bayan sun ci Garin na <strong>Zazzau<\/strong> da ya\u0199i.<\/p>\n\n\n\n<p><strong>Sarki Ali Mai<\/strong> na <strong>Daular<\/strong> <strong>Borno<\/strong>, shi ne ya taka musu birki a lokacin da suka kai wa <strong>Ngazargamu<\/strong> harin ya\u0199i kamar yadda Wikipedia (2016), ta na\u0199alto a Kundin Tarihin <strong>Katsina<\/strong> (Katsina Chronicle).<\/p>\n\n\n\n<p><strong>Jukunawa<\/strong>, mutane ne jarumai, kuma masana salo-salon ya\u0199i. Su ne suka shugabancin Daular Gamayyar Maya\u0199an <strong>Kwararrafa<\/strong>. Sun yi ya\u0199u\u0199uwan da ba za a iya \u0199ididdige yawansu ba. Sun ya\u0199i <strong>\u0198asar<\/strong> <strong>Hausa<\/strong> tun daga <strong>Dutse<\/strong> har zuwa <strong>Gobir<\/strong>. Kuma sun yi galaba a kan manya-manyan Masarautun <strong>\u0198asar Hausa<\/strong> da suka ha\u0257a da <strong>Kano<\/strong>, <strong>Katsina<\/strong> da kuma <strong>Zazzau<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p><strong>Jukunawa<\/strong> ko <strong>Kwararrafa<\/strong>, sun yi ya\u0199i na tsawon shekaru 72 da wasu daga cikin Garuruwan <strong>Hausa<\/strong>. An fara ya\u0199in tun zamanin <strong>Aku-Uka Angyu Katakpa<\/strong> daga shekarar 1599 har zuwa wa\u0257anda suka biyo bayansa a shekarar 1671, zamanin <strong>Aku-Uka<\/strong> <strong>Daju<\/strong>. Sannan kuma sun ya\u0199i Daular <strong>Borno<\/strong> a shekarar 1680 sun kuma yi galaba a kanta. Akwai wannan magana a cikin Littafin Tarihin Rayuwar (Dr.) Shekarau Angyu Masa-Ibi, Kuvyon II, wanda aka wallafa a shekarar 2016.<\/p>\n\n\n\n<p>Wannan labari na ya\u0199u\u0199uwan <strong>Jukunawa<\/strong> da manyan Masarautun <strong>\u0198asar Hausa<\/strong> ya zo a wasu Littattafan Tarihi da dama. Daga ciki akwai Marigayi Mai Martaba Sarkin Dutse, <strong>Nuhu Muhammadu Sanusi<\/strong> da ya labarta rasuwar Sarkin Dutse na 13, <strong>Mantau Jarmai<\/strong> <strong>Babba<\/strong> cewa: \u201cYa mutu a ya\u0199in <strong>Kwararrafa<\/strong> tare da wasu mutane masu yawa wa\u0257anda suka tafi ya\u0199in tare da shi.\u201d<\/p>\n\n\n\n<p>Haka nan kuma, NNPC (2007), sun labarta cewa, <strong>Kwararrafa<\/strong> ta ya\u0199i <strong>Kano<\/strong> a zamanin Sarkin <strong>Kano na 27, Muhammadu Zaki<\/strong> <strong>\u018aan<\/strong> <strong>Kiske<\/strong> (1582 \u2013 1618). Sun kuma sake ya\u0199ar Garin na <strong>Kano<\/strong> a karo na biyu zamanin Sarkin Kano na 34, M<strong>uhammadu Kukuna<\/strong> (1652 \u2013 1660). Sannan kuma suka sake komowa a karo na hu\u0257u zamanin Sarkin Kano na 36, <strong>Da\u0257i \u018aan Bawa<\/strong> (1670 \u2013 1703). A dukkan wa\u0257annan ya\u0199u\u0199uwa guda uku da aka ambata, ruwayar ta nuna an galabci <strong>Kano<\/strong> ne matu\u0199ar galaba ta in da har ta kai ga Sarakunan na <strong>Kano<\/strong> sun gudu sun bar Garin.<\/p>\n\n\n\n<p>A \u0257aya daga cikin irin wa\u0257annan ya\u0199u\u0199uwa ne su <strong>Kwararrafawa<\/strong> suka ja wa Sarkin <strong>Kano<\/strong> kunne cikin harshensu na <strong>Jukunanci<\/strong> da cewa \u201cIri ya Kasen,\u201d wanda daga baya aka jirkita shi ya zama sunan wata unguwa a garin na <strong>Kano<\/strong> mai suna <strong>Yakasai<\/strong>. Ma\u2019anar waccar kalma ta <strong>Jukunawa<\/strong> ita ce; \u201cZa mu dawo.\u201d<\/p>\n\n\n\n<p>Haka nan kuma, akwai wata Unguwa a cikin Birnin <strong>Zazzau<\/strong> mai suna <strong>Tudun Jukun<\/strong>, wacce ake dangata ta da share-wuri-zauna da su Jukunawan suka yi bayan sun ci Birnin na <strong>Zazzau<\/strong> da ya\u0199i.<\/p>\n\n\n\n<p>Babbar manufar <strong>Kwararrafa<\/strong> ta yin wa\u0257ancan ya\u0199u\u0199uwa ita ce, tabbatar da adalci ba fa\u0257a\u0257a Daula ba. Ga abin da Aku-Uka ya fa\u0257i a cikin Littafin tarihinsa: \u201cYa kamata a san cewa, <strong>Jukunawa<\/strong> ba su ya\u0199i biranen <strong>\u0198asar Hausa<\/strong> da manufar gudanar da Mulkin-Mallaka na har abada ba, sai don su nuna musu cewa akwai Maza bisa kansu\u201d Adamu (2016).<\/p>\n\n\n\n<p>Sannan kuma ya ci gaba da cewa, \u201cIya tsawon tarihin ya\u0199u\u0199uwan da kakanninmu suka yi da <strong>\u0198asar Hausa<\/strong>, ba su ta\u0253a kwasar Ganima daga can <strong>\u0198asar<\/strong> <strong>Hausa<\/strong> sun zo da ita matsugunninsu da yake \u0199asan Kogin Binuwai ba.\u201d<\/p>\n\n\n\n<p>A bisa wa\u0257annan hujjoji za mu ta\u0199aita rubutun da cewa, lallai Tarihi ya nuna an yi wa\u0257annan ya\u0199u\u0199uwa, kuma daga cikin abubuwan da suka faru, za mu iya fahimtar gaskiyar maganar zamowar <strong>Jukunawa<\/strong> mutane Jarumai masu dabarar ya\u0199i.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>Yawan Jama\u2019a<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Duk da ba wani cikakken \u0199ayadadden adadin yawan Jama\u2019ar <strong>Jukunawa<\/strong>, amma dai ana hasashen yawansu ya haura miliyan biyu da rabi (Shishi, 2014).<\/p>\n\n\n\n<p>Tun da fari, garin <strong>Wukari<\/strong> an kafa shi ne Unguwa-unguwa, wanda kuma kowace Unguwa mazauna cikinta kusan zuriya guda ce. daga cikin irin wannan Unguwanni akwai <strong>Go-Ndoku<\/strong>, wacce ke nufin &#8216;Gidan Sarki ko Fadar Sarki.&#8217; Sai kuma wasu unguwannin da suka ha\u0257a da: <strong>Kinda Kuvyo<\/strong>, <strong>Adikyu-Gashi<\/strong>, <strong>Ndo Abonta<\/strong>, <strong>Kwanse<\/strong>, <strong>Ndo-Nwugye<\/strong>, <strong>Tsupando<\/strong>, da sauransu (Adamu, 2016).<\/p>\n\n\n\n<p>Gari ne wanda ke kewaye da <strong>Ganuwa<\/strong> da kuma \u0198ofofi guda bakwai duk da cewa a yanzu, \u0198ofar Arewa ce ka\u0257ai ta saura da jama\u2019a ke amfani da ita; wacce kuma a zamanin baya, mafita ce ta gawarwakin jinin sarauta. Haka nan kuma, a tsakiyar garin akwai tsohuwar kasuwar da tun da aka kafa garin take.<\/p>\n\n\n\n<p>Sahun farko na sauran yarurruka mazauna wannan Gari na <strong>Wukari<\/strong> akwai <strong>Gobirawa<\/strong>, wa\u0257anda kasuwanci ya kai su garin kuma suke zaune kusa da Fadar Sarki, wanda har ta kai ga shugabansu mai suna &#8216;<strong>Maiwuya<\/strong>&#8216; ya auri \u01b4ar Sarkin Wukari na wancan lokacin, abin da ya ba shi damar da aka yi masa &#8216;Sarkin Kasuwar Wukari, wanda ke da alhakin tattara Haraji.<\/p>\n\n\n\n<p>Haka nan kuma a shekarar 1932, a zamanin <strong>Aku Amadu Agbumanu<\/strong>, wasu jama\u2019a daga <strong>Sakkwato<\/strong> sun \u0199aura zuwa Wukari, biyo bayan tu\u0253e <strong>Sarkin Musulmi<\/strong> <strong>Muhammadu Tambari<\/strong> da aka yi, wanda kuma ya yi Gudun Hijira zuwa garin na Wukari, in da a can ya rasu kuma aka binne shi a can. A yanzu haka sauran zuriyarsa su na zaune a wannan gari na <strong>Wukari<\/strong> a wata Unguwa da ake kira Unguwar <strong>Sakkwato<\/strong> wacce ke daura da <strong>Akata<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>Bayan zamowar wannan Gari na <strong>Wukari<\/strong> Hedikwatar Masarautar <strong>Jukunawa<\/strong>, shi ne kuma Hedikwatar \u0198aramar Hukumar <strong>Wukari<\/strong> a \u0199ar\u0199ashin Jihar <strong>Taraba<\/strong>. Yanzu haka wannan Gari ya na da ci gaban da har ta kai ga ya na da Jam\u2019o\u2019i guda uku da kuma sauran manya da \u0199ananan Makarantu.<\/p>\n\n\n\n<p>Daga farkon kafa wannan Gari zuwa yau, Sarakuna 24 ne suka shugabance shi. na farkonsu shi ne <strong>Angyu Katakpa<\/strong> (1596 \u2013 1615), sai kuma na \u0199arshe wanda har yanzu yake kai, <strong>Manu Ishaku Adda Ali<\/strong> (2022 zuwa yau).<\/p>\n\n\n\n<div class=\"wp-block-media-text is-stacked-on-mobile\"><figure class=\"wp-block-media-text__media\"><img loading=\"lazy\" decoding=\"async\" width=\"683\" height=\"1025\" src=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/fb_img_17579817643563351900827468658122-683x1025.jpg\" class=\"wp-image-3977 size-full\" srcset=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/fb_img_17579817643563351900827468658122-683x1025.jpg 683w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/fb_img_17579817643563351900827468658122-200x300.jpg 200w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/fb_img_17579817643563351900827468658122-768x1152.jpg 768w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/fb_img_17579817643563351900827468658122-1024x1536.jpg 1024w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/fb_img_17579817643563351900827468658122-600x900.jpg 600w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/fb_img_17579817643563351900827468658122.jpg 1333w\" sizes=\"(max-width: 683px) 100vw, 683px\" \/><\/figure><div class=\"wp-block-media-text__content\">\n<p><em>Aku-Uka Manu Ishaku Adda Ali. <\/em><\/p>\n<\/div><\/div>\n\n\n\n<p>Har ila yau, <strong>Jukunawa<\/strong> su na zaune cikin garuruwa da dama a jihohin <strong>Taraba<\/strong>, <strong>Binuwai<\/strong>, <strong>Nassarawa<\/strong>, <strong>Kano<\/strong>, <strong>Kaduna<\/strong>, <strong>Katsina<\/strong>, <strong>Filato<\/strong>, <strong>Adamawa<\/strong>, <strong>Gombe<\/strong> da sauran wasu garuruwan a wasu jihohin da yawansu ya kai kusan jihohi 22 a <strong>Najeriya<\/strong> da kuma wani yanki na Arewa maso yammacin \u0198asar <strong>Kamaru<\/strong> (North Western Cameroon).<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>AL\u2019ADU<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Daga cikin manya-manyan al\u2019adun <strong>Jukunawa<\/strong>, akwai al\u2019ada mai suna &#8216;<strong>Ukenho<\/strong>,&#8217; wacce ake gudanar da ita a \u0199arshen shekara. Sannan kuma akwai &#8216;<strong>Ungu<\/strong>,&#8217; da sauransu.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>ZA\u0181EN SARKIN JUKANAWA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>A al\u2019adance, idan aka samu gurbi a Fadar <strong>Jukunawa<\/strong>, sakamakon mutuwa ko wani dalili na daban, Dattawa masu za\u0253en Sarki za su bayar da umarni ga Gidajen Sarautar <strong>Jukunawa<\/strong> guda biyu; wato zuriyar <strong>Bagya<\/strong> da ta <strong>Bama<\/strong>, cewa su fitar da sunayen wa\u0257anda suke ganin su suka cancanta su nemi wannan kujera ta Sarautar <strong>Jukunawa<\/strong>. Idan suka samu wa\u0257annan sunaye, sai kuma su bi matakan da aka saba da su wajen za\u0253e da kuma na\u0257in sabon Sarki kamar haka:<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>DAREN LITININ<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Matakin farko daga cikin jerin matakan da Dattawan <strong>Jukunawa<\/strong> ke bi wajen za\u0253en sabon Sarki shi ne, kwana a garin <strong>Adi Bakundi<\/strong> a Daren Litinin da su masu neman kujerar suke yi. A wannan mataki ana umartar dukkan masu sha\u2019awar neman wannan kujera ta <strong>Aku-Uka<\/strong> su fita daga Garin <strong>Wukari<\/strong> zuwa garin <strong>Adi<\/strong> <strong>Bakundi<\/strong> a Daren Litinin, su kwana a can.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>ZA\u0181E<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Bayan an kwana \u0257aya a <strong>Adi Bakundi<\/strong>, sai kuma a ayyana wata rana guda \u0257aya da za a yi za\u0253en sarkin a cikinta. Idan ranar ta zo, sai su wa\u0257annan \u01b4an takara da suka kwana a <strong>Adi Bakundi<\/strong> su rankaya zuwa wani wuri da ake kira &#8216;<strong>Avi<\/strong>.&#8217;<\/p>\n\n\n\n<p>A wannan wuri dukkan \u01b4an takarar za su yi shigar fararen kaya (Zani da hula). Wannan shiga ana kiranta da <strong>Nbufyo<\/strong> a harshen <strong>Jukunanci<\/strong>. Bayan sun yi wannan shiga sai kuma a za\u0253i \u0257aya daga cikinsu bisa la\u2019akari da wa\u0257annan siffofin da za a zayyana.<\/p>\n\n\n\n<p>Babban abin da Dattawa masu za\u0253en Sarkin <strong>Jukun<\/strong> suke lura da shi, shi ne halaye na gari wa\u0257anda dama tun samartakar \u01b4a\u01b4an Sarki ake lura da wa\u0257annan halaye tare da su. Daga ciki akwai:<\/p>\n\n\n\n<ol class=\"wp-block-list\">\n<li>Kawo arzi\u0199i da wadata a dukkan fa\u0257in \u0199asar Jukun: Dattawan su na lura da cewa, dukkan \u018aansarki da za a za\u0253a zai kawo \u0199aruwar arzi\u0199i da wadata ta hanyar samun Damina mai yawan ruwan da zai samar da Kaka mai albarka, zaman lafiya, ha\u0257in kai da kuma kwanciyar hankali.<\/li>\n\n\n\n<li>Sannan \u018aansarkin ya zamo mai gujewa aikata laifuffuka.<\/li>\n\n\n\n<li>Ya zamo mai girmama na gaba da shi.<\/li>\n\n\n\n<li>Ya zamo mai tattali da kuma kiyaye shigar al\u2019ada ta Sarauta.<\/li>\n\n\n\n<li>Ya zamo mai kyawawan halayen da za su zama abin koyi a rayuwarsa ta Sarauta da kuma \u0257ai\u0257aiku.<\/li>\n<\/ol>\n\n\n\n<p>Idan suka laluba suka tabbatar da wa\u0257annan halaye a tare da \u0257aya daga cikinsu, wanda dama kamar yadda aka ambata tun samartakarsu ake lura da su, to sai a ayyana shi a matsayin za\u0253a\u0253\u0253en &#8216;<strong>Aku-Uka<\/strong>.&#8217;<\/p>\n\n\n\n<p>Daga nan kuma sai abubuwa su ci gaba kamar haka:<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>ZIYARAR \u018aAKIN BAUTA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Bayan an za\u0253i sabon <strong>Aku-Uka<\/strong>, sai kuma ya yi shigar &#8216;Ba\u0199a\u0199en Kaya&#8217; shi ka\u0257ai. Zai \u0257aura Ba\u0199in Zani sannan ya sanya Ba\u0199ar Hula. Sai kuma ya shiga \u018aaki mai tsarki da ake kira &#8216;<strong>Kunvyi<\/strong>&#8216; a Jukunanci.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>ZA\u0181EN SUNA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Bayan zaman sabon <strong>Aku-Uka<\/strong> a \u018aaki mai Tsarki, sai kuma ya hau Farin Doki daga Garin <strong>Avyi<\/strong> ya tafi <strong>Kuntsa<\/strong>. A wannan Gari na <strong>Kuntsa<\/strong> ne zai zauna a kan fatar Damisa, a kawo masa sunayen da sai <strong>Aku-Uka<\/strong> ne ka\u0257ai yake amsa su, ya za\u0253i guda \u0257aya daga ciki.<\/p>\n\n\n\n<p>Sunayen su ne: <strong>Agbumanu<\/strong>, <strong>Awudumanu<\/strong>, <strong>Ahumanu<\/strong>, da kuma <strong>Kuvyon<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p><strong>Kuntsa<\/strong>, suna ne na babban shugaba mai tsarki, wanda yake bai wa <strong>Aku-Uka<\/strong> wa\u0257ancan sunaye ya za\u0253i \u0257aya daga ciki, sannan kuma bayan ya za\u0253a ya dam\u0199a masa kayayyakin sirrin Sarauta (Kamar a ce tagwayen masu da ake bayar wa a Kano), wa\u0257anda mai ri\u0199e da su shi ne Sarki.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>ZA\u0181EN MATA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>A bisa al\u2019adar <strong>Jukunawa<\/strong>, za\u0253a\u0253\u0253en Sabon Sarki ya na gadar \u0257aya daga cikin matan tsohon sarkin da ya gada idan har mutuwa ya yi. Wannan al\u2019ada kuma ana gudanar da ita a <strong>Garin Puje<\/strong>. Wannan mata ita ake kira &#8216;<strong>Wakuku<\/strong>.&#8217;<\/p>\n\n\n\n<p>Saboda haka, bayan an kammala dukkanin ayyukan al\u2019ada da ya kamata a yi a Kuntsa, sai kuma Sarki da tawagarsa su zarce zuwa <strong>Puje<\/strong>, a nan za a fito masa da matan tsohon sarkin ya za\u0253i guda \u0257aya daga ciki wacce za ta zamar masa Uwar-gida.<\/p>\n\n\n\n<p>Hikimarsu ta yin wannan al\u2019ada ita ce; ita wannan Mata ta tsohon Sarki, ta ri ga ta zauna a Gidan Sarauta tare da Tsohon Sarki, saboda haka ta koyi zama da Sarki, su kuma Matan Sabon Sarkin da za su shigo ba su da wannan gogayya, saboda haka, ita sai ta koyar da su yadda ake kula da Sarki, da kuma zaman Gidan Sarauta.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>SHIGA FADA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Mataki na \u0199arshe a jerin abubuwan da ake yi a za\u0253en Sarkin <strong>Jukunawa<\/strong> shi ne, shigar Sarki Fada. Bayan Sarki ya za\u0253i Mata daga cikin Matan Tsohon Sarki, sai Matar ta kintsa kayanta ta baro Puje zuwa Wukari, idan ta zo ita za ta tarbi Sarki tare da sauran masu ri\u0199e da Sarautun Gargajiya na <strong>Jukunawa<\/strong> a wani bigire da ake kira &#8216;<strong>Afyin Acio<\/strong>.&#8217;<\/p>\n\n\n\n<p>Daga nan kuma sai sabon <strong>Aku-Uka<\/strong> ya zarce zuwa wani wajen bauta domin gudanar da ziyarar ban girma ga Allansu mai suna &#8216;<strong>Yaku<\/strong>.&#8217; Shi Yaku, shi ne Allan da yake bai wa <strong>Jukunawa<\/strong> kariya a lokutan yunwa da kuma annoba.<\/p>\n\n\n\n<p>Bayan an kammala wannan ziyarar ban girma, sai kuma sabon <strong>Aku-Uka<\/strong> ya shiga Fadarsa ta Mulki da take a Babban Birnin <strong>Jukunawa<\/strong> wato &#8216;<strong>Wukari<\/strong>.&#8217;<\/p>\n\n\n\n<p>Wannan shi ne abin da aka saba da shi a tsarin na\u0257in Sarautar <strong>Jukanawa<\/strong> a bisa turbar kaka-da-kakanni.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>BAYAN ZUWAN TURAWA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p>Da Bature ya zo ya kafa mulkinsa na mallaka a wannan \u0198asa ta <strong>Najeriya<\/strong>, sai yanayi da tsarin yadda ake gudanar da za\u0253e da na\u0257in Sarakuna ya sauya. Wannan sauyi ya shafi <strong>Jukunawa<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>Kundin Tsarin Mulkin <strong>Najeriya<\/strong> yanzu ya bai wa Gwamnan Jiha damar amincewa da kuma watsi da sunan sarkin da masu za\u0253en sabon Sarki suka mi\u0199a masa. Saboda haka, sai aka samu \u0199arin matakai guda biyu a bisa yadda aka saba, da farko akwai mi\u0199a sunan sarkin ga Gwamnatin Jiha domin tantancewa da zarar an za\u0253a, sai kuma na\u0257i bayan an kammala gudanar da wa\u0257ancan al\u2019adu da aka ambata a sama.<\/p>\n\n\n\n<p>Idan masu za\u0253en sabon <strong>Uka-Uka<\/strong> suka za\u0253e shi, to za su tura sunan zuwa ga Gwamnan Jihar <strong>Taraba<\/strong> ke nan a yau. Idan Gwamnan ya kar\u0253i wannan suna, shi ke nan sai a ci gaba da gudanar da wa\u0257ancan al\u2019adu da aka ambata a sama.<\/p>\n\n\n\n<p>Sai kuma, mata\u0199i na \u0199arshe da ya ta\u0253a wancan tsohon tsari wanda shi ne na na\u0257i. Bayan an kammala dukkan wa\u0257ancan shagulgula, sai kuma gwamna ya zo ya rantsar da Sarki a Fadarsa.<\/p>\n\n\n\n<p>Wa\u0257annan su ne abubuwa biyu da suka shigo cikin sabgar za\u0253e da na\u0257in sabon Sarki wato &#8216;<strong>Aku-Uka<\/strong>&#8216; a \u0198asar <strong>Jukunawa<\/strong>.<\/p>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>MAJALISAR SARKIN JUKUNAWA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<div class=\"wp-block-media-text is-stacked-on-mobile\"><figure class=\"wp-block-media-text__media\"><img loading=\"lazy\" decoding=\"async\" width=\"1025\" height=\"769\" src=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukunwukaripalace6369802203539650856-1025x769.jpg\" class=\"wp-image-3978 size-full\" srcset=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukunwukaripalace6369802203539650856-1025x769.jpg 1025w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukunwukaripalace6369802203539650856-300x225.jpg 300w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukunwukaripalace6369802203539650856-768x576.jpg 768w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukunwukaripalace6369802203539650856-1536x1152.jpg 1536w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukunwukaripalace6369802203539650856-600x450.jpg 600w, https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukunwukaripalace6369802203539650856.jpg 2000w\" sizes=\"(max-width: 1025px) 100vw, 1025px\" \/><\/figure><div class=\"wp-block-media-text__content\">\n<p><em>Fadar Masarautar Wukari<\/em>. <\/p>\n<\/div><\/div>\n\n\n\n<p>Majalisar Sarki; wato Majalisar <strong>Aku-Uka<\/strong>, Majalisa ce da ta \u0199unshe da mutane guda biyar; shi <strong>Aku-Uka<\/strong> (Sarki) kansa, <strong>Abon<\/strong> <strong>Acio<\/strong> (Waziri), <strong>Abon Ziken<\/strong> (Galadima), <strong>Kinda Acio<\/strong> (Sarkin Gida) da kuma <strong>Kinda<\/strong> <strong>Ziken<\/strong> (Sarkin Bai).<\/p>\n\n\n\n<ol class=\"wp-block-list\">\n<li>Aku-Uka: Shi ne kankat a Masarautar Jukun. Matsayinsa ne sama da kowane mu\u0199ami. Shi ne mai shiga tsakanin Allolin Jukunawa da kuma sauran al\u2019ummar Jukunawa. Shi ka\u0257ai yake iya magana da Allolin Jukunawa sannan ya sanar da mabiya abin da ya dace.<\/li>\n\n\n\n<li>Abon Acio (Waziri): Shi yake da ikon gudanar da duk wani aiki da Aku-Uka zai yi matu\u0199ar Aku-Uka \u0257in ba ya nan ko kuma ya na halin rashin lafiyar da za ta hana shi gudanar da Fada. Sannan shi ke bai wa Sarki shawara a harkokin al\u2019adu da kuma al\u2019amuran yau-da-kullum. Ya na da damar gudanar da shari\u2019ar da ta shafi Auratayya kai-tsaye ba tare da ya tuntu\u0253i Sarki ba. Amma kuma duk da haka, Waziri ba ya gadon kujerar Aku-Uka.<\/li>\n\n\n\n<li>Abon Ziken (Galadima): Galadima shi ne mataimakin Waziri, sannan kuma mai gadon kujerarsa da zarar babu kowa a kanta. Ya na taimaka wa Waziri wajen gudanar da ayyukan da suka shafi Sarauta.<\/li>\n\n\n\n<li>Kinda Acio (Sarkin gida): Shi ne mai kula da al\u2019amuran cikin Gidan Aku-Uka. Ya na kuma aiwatar da wasu ayyukan na fannin Sarauta, sannan kuma ya na da mataimaka masu ri\u0199e da \u0199ananan mu\u0199aman Sarauta.<\/li>\n\n\n\n<li>Kinda Ziken (Sarkin Bai): Shi ne shugaban masu ri\u0199e da \u0199ananan mu\u0199aman Sarauta.<\/li>\n<\/ol>\n\n\n\n<p>\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0\u00a0 <strong>SARAKUNAN JUKUNAWA<\/strong> <\/p>\n\n\n\n<p><em>Sarakunan Farko (Kafin 1833 \u2013 tarihin baka)<\/em><\/p>\n\n\n\n<ol class=\"wp-block-list\">\n<li><strong>Angyu Katakpa Agbukenjo (1596\u20131607)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Agwabi Agbukenjo (bayan Katakpa, \u0199arni na 17)<\/strong><\/li>\n<\/ol>\n\n\n\n<p>Wa\u0257annan sunayen biyu ne suka fi fitowa a tarihi; sauran sarakunan da suka biyo baya kafin 1833, babu wasu cikakkun bayanai masu madogara, ana samun su ne a al\u2019adun Baka na Jukun<\/p>\n\n\n\n<p><strong>Sarakunan Zamani (1833 zuwa yau)<\/strong><\/p>\n\n\n\n<ol class=\"wp-block-list\">\n<li><strong>Zikenyu Tsokwa Tasefu (1833\u20131845)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Agbumanu I Agbu (1845\u20131860)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Ashumanu II Jibo Kindonya (1860\u20131871)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Awudumanu I Abite (1871\u20131903)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Agbumanu II Agbunshu (1903\u20131915)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Ashumanu III Ali (1915\u20131927)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Agbumanu III Amadu (1927\u20131940)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Ashumanu IV Angyu Masa Ibi (1940\u20131945)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Agbumanu IV Atoshi (1945\u20131960)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Ashumanu V Adi Byewi (1960\u20131970)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Awudumanu II Abe Ali (1970\u20131974)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Agbumanu V Adda Ali (1974\u20131976)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Shekarau Angyu Masa-Ibi Kuvyon II (1976\u20132021)<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Manu Ishaku Adda Ali (2022\u2013yanzu)<\/strong><\/li>\n<\/ol>\n\n\n\n<p>&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp; <strong>MADOGARA<\/strong><\/p>\n\n\n\n<ul class=\"wp-block-list\">\n<li><strong>Wikipedia<\/strong><\/li>\n<\/ul>\n\n\n\n<ul class=\"wp-block-list\">\n<li><strong>Rumbunilimi<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Adamu \u018a. A. (2016). Shekarau Angyu Masa-Ibi, An Autobiography of the 24th Aku-Uka, as Told to \u018aanjuma A. Adamu. An buga a Able Productions tare da ha\u0257in Guiwar Animation Books<\/strong>.<\/li>\n\n\n\n<li><strong>Oluyede I.O. (1996). Shaped by Destiny, A Biography of (Dr.) Shekarau Angyu Masa-Ibi, Kuvyo II, The Aku Uka of Wukari. University of Ilorin.<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Tattaunawa da (Dr.) Shekarau Angyu, Masa-Ibi, Kuvyo II, Aku Uka na Wukari, a ranar Asabar 19\/08\/2017, a Fadarsa da ke Wukari.<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>David M.A. (2013). Ebira Youth Forum Association (E.Y.F.A). An ciro a shekarar 2016, daga shafin: http:\/\/ebirayouthforumassociation.blogspot.com.ng \/2013\/05\/history-of-ebira-people.html<\/strong>. <\/li>\n\n\n\n<li><strong>Dawuda G.A. (2011). Are The Jukuns Jews? Nigerian Masterweb Citizen News. An ciro a shekarar 2016, daga shafin:http:\/\/nigeriamasterweb.com\/blog\/index.php\/2011\/06\/ 04\/are-nigeria-s-jukuns-jews<\/strong>. <\/li>\n\n\n\n<li><strong>Mac-Leva F. (2009). Nigeria: How Giant Crocodiles Guided Jukun to Kwararafa. Daily Trust. An ciro a chekarar 2016, daga shafi: http:\/\/allafrica.com\/stories\/200906240052.html Northern Nigerian Publishing Company. (1970). Hausawa da Ma\u0199wabtansu, Littafi na Biyu. Northern Nigerian Publishing Company, Zariya \u2013 Najeriya.<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Okunna, E da Gausa, S. (2014). Adapting the Jukun Traditional Symbols for Textile Design and Production. Mgbakoigba: Journal of African Studies. Vol. 3. July, 2014<\/strong>. <\/li>\n\n\n\n<li><strong>Sanusi N. M. (2009). Stories of Dutse Palace 1421 \u2013 2009. An buga wannan littafi a ma\u0257aba\u2019ar jihar Jigawa.<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li> <strong>Ujorha T. (2012). Did the Jukun originate from Egypt? Daily Trust. An ciro a shekarar 2016, daga shafin:http:\/\/www.dailytrust.com.ng\/weekly\/index.php\/feature s\/1058-did-the-Jukun-originate-from-\u00e9gypt.<\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Boumo E. (2011). Factoring Inter-Group Relations In The Lower Benue Valley To Circa 1900 A.D. Department of History, Benue State University Makurdi, Benue State, Nigeria. African Journal of Arts and Cultural Studies Volume 4, Number 2, 2011. <\/strong><\/li>\n\n\n\n<li><strong>Dinslage S. and Leger R. (1996). Language And Migration The Impact Of The Jukun On Chadic Speaking Groups In The Benue-Gongola Basin. Berichte des Sonderforschungsbereichs 268, Band 8, Frankfurt a. M. 1996: 67-75<\/strong>. <\/li>\n\n\n\n<li><strong>Edo V. O. (2008). The Evolution and Development of Central Administration in Ebiraland, 1920-1997. An ciro a shekarar 2016, daga shafin: http:\/\/www.nobleworld.biz\/images\/Edo.pdf<\/strong>. <\/li>\n\n\n\n<li><strong>Okpeh O.O. da Ochefu Y.A. (Babu Lokacin Bugu). The Idoma Ethnic Group: A Historical And Cultural Setting.<\/strong><\/li>\n<\/ul>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Wukari, kamar yadda aka fi kiranta, ita ce Hedikwatar Masarautar Wukari. Asalin sunanta shi ne &#8216;Ukari,&#8217; wacce kuma kalma ce ta Jukunanci, wacce ke da ma\u2019anar; &#8216;Ka fifita&#8217; (you have surpassed). Masarauta ce da aka kafa ta a shekarar 1596 bayan rushewar Daular Kwararrafa. &nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp; TUSHE Bayan rushewar Daular Kwararrafa wacce ke da Hedikwata a [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":3981,"comment_status":"open","ping_status":"open","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"inline_featured_image":false,"_jetpack_memberships_contains_paid_content":false,"footnotes":""},"categories":[94],"tags":[122],"class_list":["post-3975","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-masarautu","tag-masarautarwukari-jukunawa-aku-uka-masarautu"],"yoast_head":"<!-- This site is optimized with the Yoast SEO plugin v27.0 - https:\/\/yoast.com\/product\/yoast-seo-wordpress\/ -->\n<title>Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya<\/title>\n<meta name=\"robots\" content=\"noindex, follow, max-snippet:-1, max-image-preview:large, max-video-preview:-1\" \/>\n<meta property=\"og:locale\" content=\"en_US\" \/>\n<meta property=\"og:type\" content=\"article\" \/>\n<meta property=\"og:title\" content=\"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya\" \/>\n<meta property=\"og:description\" content=\"Wukari, kamar yadda aka fi kiranta, ita ce Hedikwatar Masarautar Wukari. Asalin sunanta shi ne &#8216;Ukari,&#8217; wacce kuma kalma ce ta Jukunanci, wacce ke da ma\u2019anar; &#8216;Ka fifita&#8217; (you have surpassed). Masarauta ce da aka kafa ta a shekarar 1596 bayan rushewar Daular Kwararrafa. &nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp; TUSHE Bayan rushewar Daular Kwararrafa wacce ke da Hedikwata a [&hellip;]\" \/>\n<meta property=\"og:url\" content=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975\" \/>\n<meta property=\"og:site_name\" content=\"Taskar Nasaba\" \/>\n<meta property=\"article:published_time\" content=\"2025-09-21T12:13:16+00:00\" \/>\n<meta property=\"article:modified_time\" content=\"2025-09-21T12:15:20+00:00\" \/>\n<meta property=\"og:image\" content=\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129.jpeg\" \/>\n\t<meta property=\"og:image:width\" content=\"2000\" \/>\n\t<meta property=\"og:image:height\" content=\"1500\" \/>\n\t<meta property=\"og:image:type\" content=\"image\/jpeg\" \/>\n<meta name=\"author\" content=\"Salahuddeen Muhammad\" \/>\n<meta name=\"twitter:card\" content=\"summary_large_image\" \/>\n<meta name=\"twitter:label1\" content=\"Written by\" \/>\n\t<meta name=\"twitter:data1\" content=\"Salahuddeen Muhammad\" \/>\n\t<meta name=\"twitter:label2\" content=\"Est. reading time\" \/>\n\t<meta name=\"twitter:data2\" content=\"23 minutes\" \/>\n<script type=\"application\/ld+json\" class=\"yoast-schema-graph\">{\"@context\":\"https:\/\/schema.org\",\"@graph\":[{\"@type\":\"Article\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#article\",\"isPartOf\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975\"},\"author\":{\"name\":\"Salahuddeen Muhammad\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/person\/44e1eb0350c3f1b57f525e9d3ebe4753\"},\"headline\":\"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya\",\"datePublished\":\"2025-09-21T12:13:16+00:00\",\"dateModified\":\"2025-09-21T12:15:20+00:00\",\"mainEntityOfPage\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975\"},\"wordCount\":4621,\"commentCount\":0,\"publisher\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#organization\"},\"image\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage\"},\"thumbnailUrl\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg\",\"keywords\":[\"#masarautarwukari #jukunawa #aku-uka #masarautu\"],\"articleSection\":[\"Masarautu\"],\"inLanguage\":\"en-US\",\"potentialAction\":[{\"@type\":\"CommentAction\",\"name\":\"Comment\",\"target\":[\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#respond\"]}]},{\"@type\":\"WebPage\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975\",\"url\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975\",\"name\":\"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya\",\"isPartOf\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#website\"},\"primaryImageOfPage\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage\"},\"image\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage\"},\"thumbnailUrl\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg\",\"datePublished\":\"2025-09-21T12:13:16+00:00\",\"dateModified\":\"2025-09-21T12:15:20+00:00\",\"breadcrumb\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#breadcrumb\"},\"inLanguage\":\"en-US\",\"potentialAction\":[{\"@type\":\"ReadAction\",\"target\":[\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975\"]}]},{\"@type\":\"ImageObject\",\"inLanguage\":\"en-US\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage\",\"url\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg\",\"contentUrl\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg\",\"width\":360,\"height\":263},{\"@type\":\"BreadcrumbList\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#breadcrumb\",\"itemListElement\":[{\"@type\":\"ListItem\",\"position\":1,\"name\":\"Home\",\"item\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/\"},{\"@type\":\"ListItem\",\"position\":2,\"name\":\"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya\"}]},{\"@type\":\"WebSite\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#website\",\"url\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/\",\"name\":\"Taskar Nasaba\",\"description\":\"\",\"publisher\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#organization\"},\"potentialAction\":[{\"@type\":\"SearchAction\",\"target\":{\"@type\":\"EntryPoint\",\"urlTemplate\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?s={search_term_string}\"},\"query-input\":{\"@type\":\"PropertyValueSpecification\",\"valueRequired\":true,\"valueName\":\"search_term_string\"}}],\"inLanguage\":\"en-US\"},{\"@type\":\"Organization\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#organization\",\"name\":\"Taskar Nasaba\",\"url\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/\",\"logo\":{\"@type\":\"ImageObject\",\"inLanguage\":\"en-US\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/logo\/image\/\",\"url\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2026\/02\/cropped-TN_WHITE.jpg-removebg-preview.png\",\"contentUrl\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2026\/02\/cropped-TN_WHITE.jpg-removebg-preview.png\",\"width\":343,\"height\":345,\"caption\":\"Taskar Nasaba\"},\"image\":{\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/logo\/image\/\"}},{\"@type\":\"Person\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/person\/44e1eb0350c3f1b57f525e9d3ebe4753\",\"name\":\"Salahuddeen Muhammad\",\"image\":{\"@type\":\"ImageObject\",\"inLanguage\":\"en-US\",\"@id\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/person\/image\/\",\"url\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2024\/11\/IMG-20191129-WA0036-100x100.jpg\",\"contentUrl\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2024\/11\/IMG-20191129-WA0036-100x100.jpg\",\"caption\":\"Salahuddeen Muhammad\"},\"description\":\"\u018aanjarida, marubuci, mai manufar bun\u0199asa harshen Hausa da al'adar da ba ta yi karan-tsaye a addini ba.\",\"sameAs\":[\"https:\/\/taskarnasaba.com\"],\"url\":\"https:\/\/taskarnasaba.com\/?author=1\"}]}<\/script>\n<!-- \/ Yoast SEO plugin. -->","yoast_head_json":{"title":"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya","robots":{"index":"noindex","follow":"follow","max-snippet":"max-snippet:-1","max-image-preview":"max-image-preview:large","max-video-preview":"max-video-preview:-1"},"og_locale":"en_US","og_type":"article","og_title":"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya","og_description":"Wukari, kamar yadda aka fi kiranta, ita ce Hedikwatar Masarautar Wukari. Asalin sunanta shi ne &#8216;Ukari,&#8217; wacce kuma kalma ce ta Jukunanci, wacce ke da ma\u2019anar; &#8216;Ka fifita&#8217; (you have surpassed). Masarauta ce da aka kafa ta a shekarar 1596 bayan rushewar Daular Kwararrafa. &nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp;&nbsp; TUSHE Bayan rushewar Daular Kwararrafa wacce ke da Hedikwata a [&hellip;]","og_url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975","og_site_name":"Taskar Nasaba","article_published_time":"2025-09-21T12:13:16+00:00","article_modified_time":"2025-09-21T12:15:20+00:00","og_image":[{"width":2000,"height":1500,"url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/jukun28110868753654842129.jpeg","type":"image\/jpeg"}],"author":"Salahuddeen Muhammad","twitter_card":"summary_large_image","twitter_misc":{"Written by":"Salahuddeen Muhammad","Est. reading time":"23 minutes"},"schema":{"@context":"https:\/\/schema.org","@graph":[{"@type":"Article","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#article","isPartOf":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975"},"author":{"name":"Salahuddeen Muhammad","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/person\/44e1eb0350c3f1b57f525e9d3ebe4753"},"headline":"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya","datePublished":"2025-09-21T12:13:16+00:00","dateModified":"2025-09-21T12:15:20+00:00","mainEntityOfPage":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975"},"wordCount":4621,"commentCount":0,"publisher":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#organization"},"image":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage"},"thumbnailUrl":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg","keywords":["#masarautarwukari #jukunawa #aku-uka #masarautu"],"articleSection":["Masarautu"],"inLanguage":"en-US","potentialAction":[{"@type":"CommentAction","name":"Comment","target":["https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#respond"]}]},{"@type":"WebPage","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975","url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975","name":"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya","isPartOf":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#website"},"primaryImageOfPage":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage"},"image":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage"},"thumbnailUrl":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg","datePublished":"2025-09-21T12:13:16+00:00","dateModified":"2025-09-21T12:15:20+00:00","breadcrumb":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#breadcrumb"},"inLanguage":"en-US","potentialAction":[{"@type":"ReadAction","target":["https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975"]}]},{"@type":"ImageObject","inLanguage":"en-US","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#primaryimage","url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg","contentUrl":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg","width":360,"height":263},{"@type":"BreadcrumbList","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?p=3975#breadcrumb","itemListElement":[{"@type":"ListItem","position":1,"name":"Home","item":"https:\/\/taskarnasaba.com\/"},{"@type":"ListItem","position":2,"name":"Asali da Tarihin Jukunawa: Masarautar Wukari a Idon Duniya"}]},{"@type":"WebSite","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#website","url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/","name":"Taskar Nasaba","description":"","publisher":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#organization"},"potentialAction":[{"@type":"SearchAction","target":{"@type":"EntryPoint","urlTemplate":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?s={search_term_string}"},"query-input":{"@type":"PropertyValueSpecification","valueRequired":true,"valueName":"search_term_string"}}],"inLanguage":"en-US"},{"@type":"Organization","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#organization","name":"Taskar Nasaba","url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/","logo":{"@type":"ImageObject","inLanguage":"en-US","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/logo\/image\/","url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2026\/02\/cropped-TN_WHITE.jpg-removebg-preview.png","contentUrl":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2026\/02\/cropped-TN_WHITE.jpg-removebg-preview.png","width":343,"height":345,"caption":"Taskar Nasaba"},"image":{"@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/logo\/image\/"}},{"@type":"Person","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/person\/44e1eb0350c3f1b57f525e9d3ebe4753","name":"Salahuddeen Muhammad","image":{"@type":"ImageObject","inLanguage":"en-US","@id":"https:\/\/taskarnasaba.com\/#\/schema\/person\/image\/","url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2024\/11\/IMG-20191129-WA0036-100x100.jpg","contentUrl":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2024\/11\/IMG-20191129-WA0036-100x100.jpg","caption":"Salahuddeen Muhammad"},"description":"\u018aanjarida, marubuci, mai manufar bun\u0199asa harshen Hausa da al'adar da ba ta yi karan-tsaye a addini ba.","sameAs":["https:\/\/taskarnasaba.com"],"url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/?author=1"}]}},"jetpack_featured_media_url":"https:\/\/taskarnasaba.com\/wp-content\/uploads\/2025\/09\/04e6c6c5-b6ce-4e97-b2a4-900d91225762.jpeg","jetpack_sharing_enabled":true,"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/3975","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=3975"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/3975\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":3982,"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/3975\/revisions\/3982"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/3981"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=3975"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=3975"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/taskarnasaba.com\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=3975"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}