Ku Kasance Tare da Mu!

Yi rijista don samun sabbin labaranmu nan take!

Nana Asma’u Lawal Liman

Director Operations and Evaluation

Nana Asma’u Lawal Liman
Director Operations and Evaluation

Wacce aka haifa a ranar 26 ga watan Agusta na shekarar 2002, a Ƙaramar Hukumar Ƙaura-Namoda da ke jihar Zamfara a Tarayyar Najeriya.

Ta yi karatun Firamare a Nelson Mandela International School da ke garin Abuja, yayin da ta tafi Jihar Katsina inda ta yi Sakandare a makarantar Ulul-Albab Science Secondary School.

Har wa yau, ta kuma mallaki shaidar kammala karatun Diploma (ND) a fannin Ƙere-Ƙere (Civil Engineering Technology), a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya, Ƙaura-Namoda, Zamfara.

A ɓangaren karatun addini kuwa; Ta sauke Alkur’ani mai girma a 2019, ta kuma sake sauke wa a karo na biyu a shekara ta 2021.

Ta yi aiki da wasu Jaridun yanar gizo irinsu; One News Hausa, da Bakandamiya Reading Club.

Bugu da ƙari, Nana Asma’u (Queen-Nasmah), ta kasance shahararriyar marubuciya wacce ta yi shura a Duniyar Adabi. Yanzu haka, ita ce Shugabar ƙungiyar Moonlight Writers Association.

✉️ Asmaunanalawalliman@gmail.com