A ranar 20 ga watan Ramadan, shekara ta 8 bayan Hijira (630 Miladiyya) ne Musulmai ƙarkashin jagorancin Annabi Muhammadu (SAW) suka ci garin Makka tare da rundunar Sahabbai kusan 10,000, ba tare da zubar da jini ba.
Wannan nasara ta kawo ƙarshen rikicin da aka shafe shekaru ana yi tsakanin Musulmai da Quraysh, tare da sauya Makka daga mulkin mushrikai zuwa mulkin Musulunci.
Dalilin Cin Makka
Bayan Hijirar Musulmai zuwa Madina, an yi yaƙe-yaƙe da dama tsakaninsu da Quraysh. A shekara ta 6 bayan Hijira an ƙulla Yarjejeniyar Hudaybiyah ta zaman lafiya na shekaru 10.
Sai dai, Quraysh sun karya yarjejeniyar ta hanyar taimaka wa Banu Bakr su kai hari ga Banu Khuza’ah (abokan Musulmai), har aka kashe mutane daga cikinsu. Wannan ne ya sa Annabi SAW ya shirya runduna domin tafiya Makka.
Yadda Aka Ci Makka
Rundunar Musulmai ta tashi a 10 ga Ramadan kuma ta shiga Makka cikin kwanciyar hankali. Annabi SAW ya karanta ayar Alƙur’ani:
“Gaskiya ta zo, ƙarya kuma ta gushe.” (Suratul Isra’i 17:81)
An rushe Gumaka da ke cikin Ka’aba, aka dawo da ibadar Tauhidi.
Gafarar Annabi ga Quraysh
Duk da irin azabar da suka yi wa Musulmai a baya, Annabi SAW ya gafarta musu ya na mai cewa:
“Ku tafi, kun ƴantu.”
Wannan ya nuna rahama da adalcin Musulunci, kuma bayan wannan lamari mutane da yawa suka rungumi Musulunci.
Muhimmancin Wannan Rana
Cin Makka ya zama babban juyi a tarihin Musulunci, domin ya kawo ƙarshen shirka a Ka’aba tare da fara sabon zamani na yaɗuwar Musulunci.

