Netherlands za ta Mayar wa Najeriya Kayan Tarihi da Turawa Suka Sace
Ƙasar Netherlands za ta mayar wa Najeriya mutum-mutumin Tagulla 113 da Turawan Mulkin Mallaka suka sace. An sace su ne a shekarar 1897, daga Masarautar Benin wadda yanzu take a Najeriya, inda aka rarraba su a Gidajen Ajiyar Kayan Tarihi a Netherlands. Yayin da za a rattaba hannu a yarjejeniyar mayar da kayan tarihin zuwa […]













